Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ez 16:57-62 Littafi Mai Tsarki (HAU)

57. kafin asirin muguntarki ya tonu ba? Amma yanzu kin zama abin zargi ga 'ya'yan Edom mata, da waɗanda suke kewaye da ita, da 'ya'yan Filistiyawa mata waɗanda suke kewaye, waɗanda suke raina ki.

58. Kina ɗauke da hukuncin lalatarki da na abubuwanki masu banƙyama, ni Ubangiji na faɗa.”

59. “Ni Ubangiji Allah na ce, zan yi miki yadda kika yi, ke da kika yi rantsuwar kafara, kika ta da alkawari.

60. Duk da haka zan tuna da alkawarin da na yi da ke a kwanakin kuruciyarki. Zan ƙulla madawwamin alkawari da ke.

61. Sa'an nan za ki tuna da ayyukanki, ki ji kunya, sa'ad da na ɗauki yarki da ƙanwarki, na ba ki su, su zama 'ya'yanki mata, amma ba a kan alkawarin da na yi da ke ba.

62. Zan ƙulla alkawarina da ke, za ki sani ni ne Ubangiji,

Karanta cikakken babi Ez 16