Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ez 16:15-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

15. “Amma kin dogara ga kyanki, kika yi karuwanci saboda shahararki. Kin yi ta karuwancinki da kowane mai wucewa.

16. Kin ɗauki waɗansu rigunanki, kika yi wa kanki masujadai masu ado, sa'an nan kika yi karuwanci a cikinsu, irin abin da ba a taɓa yi ba, ba kuwa za a yi ba nan gaba.

17. Kin kuma ɗauki kayan adonki na zinariyata da azurfata waɗanda na ba ki, kin yi wa kanki siffofin mutane don ki yi karuwanci da su.

18. Kin ɗauki tufafinki da aka yi musu ado, kika lulluɓe su, sa'an nan kika ajiye maina da turarena a gabansu.

19. Abincina da na ba ki kuma, wato lallausan gāri, da mai, da zuma, waɗanda na ciyar da ke da su, kin ajiye a gabansu don ƙanshi mai daɗi, ni Ubangiji Allah na faɗa.

20. “Kin kuma kwashe 'ya'yana mata da maza waɗanda kika haifa mini kin miƙa su hadaya ga gumaka. Karuwancinki, ba ƙanƙanen abu ba ne.

Karanta cikakken babi Ez 16