Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ez 14:1-5 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Waɗansu dattawa na Isra'ila suka zo wurina, suka zauna a gabana.

2. Sai Ubangiji ya yi magana da ni, ya ce,

3. “Ɗan mutum, waɗannan mutane sun sa zukatansu ga bin gumaka, sun sa abin tuntuɓe a gabansu, zan fa yarda su yi tambaya a wurina?

4. “Sai ka faɗa musu, cewa Ubangiji Allah ya ce duk mutumin Isra'ila, wanda ya manne wa gumaka, ya sa abin tuntuɓe a gabansa sa'an nan kuma ya zo wurin annabi, ni Ubangiji zan sāka masa gwargwadon yawan gumakansa,

5. domin in kama zukatan mutanen Isra'ila waɗanda suka zama baƙi a gare ni, saboda gumakansu.

Karanta cikakken babi Ez 14