Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ez 1:1-6 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. A ranar biyar ga watan huɗu, a shekara ta talatin, ina cikin waɗanda aka kai su bautar talala, muna kusa da kogin Kebar, sai aka buɗe mini sammai, na kuwa ga wahayi na ɗaukakar Allah.

2. A kan rana ta biyar ga watan, a shekara ta biyar da aka kai sarki Yekoniya bautar talala,

3. Ubangiji ya yi magana da Ezekiyel, firist, ɗan Buzi, a ƙasar Kaldiyawa, kusa da kogin Kebar. Ikon Ubangiji yana bisa kansa.

4. Da na duba, sai ga hadiri mai iska ya taso daga wajen arewa, da wani babban girgije da haske kewaye da shi, da wuta tana ta ci falfal. A tsakiyar wutar wani abu yana walƙiya kamar tagulla.

5. Daga tsakiya wutar, sai ga kamannin waɗansu talikai su huɗu. Ga irin kamanninsu, suna kama da mutane.

6. Amma kowannensu yana da fuskoki huɗu, da fikafikai huɗu.

Karanta cikakken babi Ez 1