Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Dan 7:7-16 Littafi Mai Tsarki (HAU)

7. “Bayan wannan kuma a wahayi na dare na ga dabba ta huɗu mai ƙarfi ƙwarai, mai bantsoro da banrazana. Tana da haƙoran ƙarfe, zaga-zaga. Ta cinye, ta ragargaza, sa'an nan ta tattake sauran da ƙafafunta. Dabam take da sauran dabbobin da suka riga ta. Tana kuma da ƙaho goma.

8. Ina duban ƙahonin, sai ga wani ƙaho, ɗan ƙanƙane, ya ɓullo a tsakiyarsu. Sai aka tumɓuke ƙaho uku na fari daga cikinsu. Wannan ƙaramin ƙaho yana da idanu kamar na mutum, yana kuma da baki, yana hurta maganganu na fariya.”

9. “Ina dubawa sai na ga an ajiye gadajen sarauta,Sai wani wanda yake Tun Fil Azal ya zauna kursiyinsa.Rigarsa fara fat kamar dusar ƙanƙara,Gashin kansa kamar ulu ne tsantsa,Kursiyinsa harshen wuta ne,Ƙafafun kursiyin masu kamar karusa, wuta ne.

10. Kogin wuta yana gudu daga gabansa.Dubun dubbai suna ta yi masa hidima,Dubu goma sau dubu goma suka tsaya a gabansa,Aka kafa shari'a, aka buɗe littattafai.

11. “Na yi ta dubawa saboda manya manyan maganganun fariya da ƙahon yake hurtawa, sai na ga an kashe dabbar, an jefar da gawar cikin wuta don ta ƙone.

12. Sauran dabbobi kuwa aka karɓe mulkinsu, amma aka bar su da rai har wani ƙayyadadden lokaci.

13. “A cikin wahayi na dare, na ga wani kamar Ɗan Mutum.Yana zuwa cikin gizagizai,Ya zo wurin wanda yake Tun Fil Azal,Aka kai shi gabansa.

14. Aka kuwa danƙa masa mulki, da ɗaukaka, da sarauta,Domin dukan jama'a, da al'ummai, da harsuna su bauta masa.Mulkinsa, madawwamin mulki ne,Wanda ba zai ƙare ba.Sarautarsa ba ta tuɓuwa.”

15. “Amma ni Daniyel raina ya damu, wahayin da na gani ya tsorata ni.

16. Sai na matsa kusa da ɗaya daga cikin waɗanda suke tsaye a wurin, na tambaye shi ma'anar waɗannan abubuwa duka. Sai ya bayyana mini, ya kuma ganar da ni ma'anar waɗannan abubuwa.

Karanta cikakken babi Dan 7