Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Dan 1:7-9 Littafi Mai Tsarki (HAU)

7. Sai sarkin fāda ya laƙaba musu sababbin sunaye. Ya kira Daniyel, Belteshazzar, ya kira Hananiya, Shadrak, ya kira Mishayel, Meshak, sa'an nan ya kira Azariya, Abed-nego.

8. Daniyel kuwa ya ƙudura a ransa, ba zai ƙazantar da kansa da cin abinci iri na sarki da shan ruwan inabinsa ba, don haka ya roƙi sarkin fāda, kada ya ba shi wannan abincin da zai ƙazantar da shi.

9. Allah kuwa ya sa Daniyel ya sami farin jini da soyayya a wurin sarkin fāda.

Karanta cikakken babi Dan 1