Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 6:8-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. “Me ya sa Allah ya ƙi ba ni abin da nake roƙo?Me ya sa ya ƙi yin abin da nake so?

9. Da ma ya ci gaba kawai ya kashe ni,Ko ya sake ikonsa ya datse ni!

10. Da na san zai yi haka, da sai in yi tsalle don murna,Da ba zan kula da tsananin azabar da nake ciki ba.Ban taɓa yin gāba da umarnan Allah ba.

11. Wane ƙarfi ne nake da shi na rayuwa?Wane sa zuciya kuma nake da ita,tun da na tabbata mutuwa zan yi?

12. Da dutse aka yi ni?Ko da tagulla aka yi jikina?

13. Ba ni da sauran ƙarfi da zan ceci kaina,Ba inda zan juya in nemi taimako.

14. “A cikin irin wannan wahalaIna bukatar amintattun abokai,Ko da na rabu da Allah, ko ina tare da shi.

15. Amma ku abokaina,kun ruɗe ni,Kamar rafi wanda yakan ƙafe da rani.

16-17. Rafin yana cike da iska mai laima da ƙanƙara,Amma lokacin zafi sai su ɓace,Kwacciyar rafin, sai ta bushe ba kome.

18. Ayari sukan ɓata garin neman ruwa,Su yi ta gilo, har su marmace a hamada.

19. Ayari daga Sheba da Tema suka yi ta nema,

20. Amma sa zuciyarsu ta ƙare a gefen busassun rafuffuka,

Karanta cikakken babi Ayu 6