Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 34:8-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. Wanda yake cuɗanya da ƙungiyar masu aikata laifi,Kana yawo tare da mugaye?

9. Gama ka ce, ‘Bai amfana wa mutum kome baYa yi murna da Allah.’

10. “Saboda haka ku kasa kunne gare ni, ku da kuke haziƙai,Sam, Allah ba mai aikata mugunta ba ne,A wurin Mai Iko Dukka ba kuskure,

11. Gama bisa ga aikin mutum yake sāka masa,Yana sa aniyarsa ta bi shi.

12. Gaskiya ce, Allah ba zai aikata mugunta ba,Mai Iko Dukka ba zai kauce wa adalci ba.

13. Wa ya shugabantar da shi a kan duniya?Wa ya mallakar masa da duniya duka?

14. Da zai amshe ruhu da numfashin da ya hura wa mutum,

15. Da duk mai rai ya halaka,Mutum kuma ya koma ƙura.

16. “Idan kai haziƙi ne, to, ji wannan,Kasa kunne ga abin da zan faɗa.

17. Da Allah maƙiyin adalci ne, da ya yi mallaka?Ka iya sa wa Adali, Mai Iko Dukka laifi?

18. Ka iya sa wa Allah laifi,Shi da ya ce, ‘Sarki marar amfani ne,Hakimai kuma mugaye’?

19. Ba ya nuna sonkai ga sarakuna,Ko kuma ya fi kulawa da attajira fiye da matalauta,Gama shi ya halicce su duka.

20. Sukan mutu nan da nan,Da tsakar dare manya da ƙanana sukan shuɗe farat ɗaya,An kawar da su ba da hannun mutum ba.

Karanta cikakken babi Ayu 34