Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 30:2-16 Littafi Mai Tsarki (HAU)

2. Wace riba zan samu ta wurin ƙarfin hannuwansu waɗanda ba su da sauran kuzari?

3. Saboda rashi da matsananciyar yunwa sun rame,Sai gaigayar ƙasa suke yi da dare, a cikin kufai.

4. Sukan tsinki ganyaye masu ɗaci na jeji su ci,Sukan ci doyar jeji.

5. Aka kore su daga cikin mutane,Suka yi ta binsu da ihu kamar yadda ake yi wa ɓarawo,

6. Sai a kwazazzabai suke zamaDa a ramummuka da kogwannin duwatsu.

7. Suka yi ta kuka a jeji,Suka taru wuri ɗaya a cikin sarƙaƙƙiya.

8. Mutane ne marasa hankali marasa suna!Aka kore su daga ƙasar.

9. “Yanzu na zama abin waƙa gare su,Abin ba'a kuma a gare su.

10. Suna ƙyamata, guduna suke yi,Da ganina, sai su tofa mini yau.

11. Domin Allah ya katse lakata, ya ƙasƙanta ni,Saboda haka sun raba ni da zuriyata,

12. A hannun dama 'yan tā da zaune tsaye sun taso mini,Sun runtume ni, sun tura ni a hanyarsu ta hallakarwa.

13. Sun datse hanyata,Sun jawo mini bala'i,Ba kuwa wanda ya hana su.

14. Sun kutsa kamar waɗanda suka karya doka,Sun auka mini da dukan ƙarfinsu kamar yadda suka yi nufi.

15. Sun firgita ni,Sun kori darajata kamar da iska,Wadatata kuma ta shuɗe kamar girgije.

16. “Yanzu zuciyata ta narkeKwanakin wahala sun same ni.

Karanta cikakken babi Ayu 30