Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 24:1-6 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. “Me ya sa Allah bai tsai da ranar da zai yi shari'a ba?Me ya sa ba ya tsai da ranar adalci gaWaɗanda suka bauta masa?

2. Mugaye sukan ci iyaka,Don su ƙara yawan gonarsu.Sukan saci tumaki su zuba cikin garkunansu.

3. Sukan saci jakunan marayu,Su kama san gwauruwa,Su ce sai ta biya basusuwanta.

4. Sukan hana matalauta samun halaliyarsu,Sukan tilasta wa masu bukata su gudu su ɓuya.

5. Kamar jakunan jeji waɗanda sukan nemi abinci a busasshen jeji,Haka matalauta suke,Ba inda za su iya samo wa 'ya'yansu abinci.

6. Ya zama tilas a gare su su girbe gonakin da ba nasu ba,Su tattara 'ya'yan inabi daga gonakin mugaye.

Karanta cikakken babi Ayu 24