Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 16:7-14 Littafi Mai Tsarki (HAU)

7. Ka gajiyar da ni, ya Allah,Ka shafe iyalina.

8. Ka kama ni, kai maƙiyina ne.Na zama daga fata sai ƙasusuwa,Mutane suka ɗauka, cewa wannan ya tabbatar ni mai laifi ne.

9. Allah ya kakkarya gaɓoɓina da fushinsa,Yana dubana da ƙiyayya.

10. Mutane sun buɗe baki don su haɗiye niSuna kewaye ni suna ta marina.

11. Allah ya bashe ni ga mugaye.

12. Dā ina zamana da salama,Amma Allah ya maƙare ni,Ya fyaɗa ni ƙasa ya ragargaza ni.Allah ya maishe ni abin bārata.

13. Ya harbe ni da kibau daga kowane gefe.Kiban sun ratsa jikina sun yi mini rauni,Duk da haka bai nuna tausayi ba!

14. Ya yi ta yi mini rauni a kai a kai,Ya fāɗa mini kamar soja da ƙiyayya ta haukata.

Karanta cikakken babi Ayu 16