Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 10:5-16 Littafi Mai Tsarki (HAU)

5. Kai ma ranka gajere ne kamar namu?

6. In haka ne, me ya sa kake bin diddigin dukan laifofina,Kana farautar dukan abin da na yi?

7. Ka sani, ba ni da laifi,Ka kuma sani, ba wanda zai cece ni daga gare ka.

8. “Da ikonka ne ka yi ni, ka siffata ni,Yanzu kuma da ikon nan naka ne za ka hallaka ni.

9. Ka tuna, ya Allah, kai ka halicce ni, da yumɓu kuwa ka yi ni.Za ka murtsuke ni ne, in kuma koma ƙura?

10. Kai ne ka ba mahaifina ƙarfin da zai haife ni,Kai ne ka sa na yi girma a cikin cikin mahaifiyata.

11. Kai ne ka siffata jikina da ƙasusuwa da jijiyoyi,Ka rufe ƙasusuwan da nama, naman kuma ka rufe da fata.

12. Kai ne ka ba ni rai da madawwamiyar ƙauna,Kulawarka ce ta sa ni rayuwa.

13. Amma yanzu na sani,Dukan lokacin nan kana da wani nufi a ɓoye game da ni.

14. Jira kake ka ga ko zan yi zunubi,Don ka ƙi gafarta mini.

15. Da cewa na yi zunubi, na shiga uku ke nan a wurinka.Amma sa'ad da na yi abin kirki ba na samun yabo.Ina baƙin ciki ƙwarai, kunya ta rufe ni.

16. Da zan ci nasara a kan kowane abu,Da sai ka yi ta farautata kamar zaki,Kana aikata al'ajabai don ka cuce ni.

Karanta cikakken babi Ayu 10