Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 10:15-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

15. Da cewa na yi zunubi, na shiga uku ke nan a wurinka.Amma sa'ad da na yi abin kirki ba na samun yabo.Ina baƙin ciki ƙwarai, kunya ta rufe ni.

16. Da zan ci nasara a kan kowane abu,Da sai ka yi ta farautata kamar zaki,Kana aikata al'ajabai don ka cuce ni.

17. A koyaushe kakan karɓi shaida gāba da ni,Fushinka sai gaba gaba yake yi a kaina,Kakan yi mini farmaki a koyaushe.

18. “Ya Allah, me ya sa ka bari aka haife ni?Da ma na mutu tun kafin wani ya gan ni!

19. Da a ce daga cikin cikin mahaifiyata an wuce da ni zuwa kabariDa ya fi mini kyau bisa ga kasancewata.

20. Raina bai kusa ƙarewa ba? A bar ni kawai!Bari in ci moriyar lokacin da ya rage mini.

Karanta cikakken babi Ayu 10