Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

2 Tar 26:1-3 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Dukan jama'ar Yahuza fa suka ɗauki Azariya, ɗan shekara goma sha shida, suka naɗa shi sarki, ya gāji gadon sarautar tsohonsa Amaziya.

2. Ya gina Elat, ya komar da ita ga Yahuza, bayan rasuwar sarki.

3. Azariya yana da shekara goma sha shida sa'ad da ya ci sarauta. Ya kuwa yi mulki a Urushalima shekara hamsin da biyu, sunan tsohuwarsa Yekoliya ta Urushalima.

Karanta cikakken babi 2 Tar 26