Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

2 Tar 13:1-4 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. A shekara ta goma sha takwas ta mulkin sarki Yerobowam, sai Abaija ya ci sarautar Yahuza.

2. Ya yi mulki shekara uku a Urushalima, sunan tsohuwarsa Ma'aka, 'yar Uriyel na Gibeya.Sai yaƙi ya ɓarke a tsakanin Abaija da Yerobowam.

3. Abaija ya tafi da rundunar jarumawansa, dubu ɗari huɗu (400,000) zaɓaɓɓun mutane. Yerobowam shi kuma ya jā dāgar yaƙi don ya kara da Abaija, yana da mutum dubu ɗari takwas (800,000), zaɓaɓɓun mayaƙa ƙarfafa.

4. Sai Abaija ya hau kan Dutsen Zemarayim, wanda yake a ƙasar Ifraimu mai tuddai, ya ce, “Ku kasa kunne gare ni, ya Yerobowam da dukanku Isra'ilawa.

Karanta cikakken babi 2 Tar 13