Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

2 Sar 9:4-9 Littafi Mai Tsarki (HAU)

4. Sai saurayin nan, annabin, ya tafi Ramot-gileyad.

5. Sa'ad da ya isa, sai ga shugabannin sojoji suna taro. Sai ya ce, “Ina da saƙo dominka, ya shugaba.”Yehu kuwa ya ce, “Wane ne a cikinmu?”Sai ya ce, “Kai ne, ya shugaba.”

6. Sai Yehu ya tashi ya shiga ɗaki, saurayin kuwa ya zuba masa mai a ka, ya ce, “Ubangiji, Allah na Isra'ila, ya keɓe ka sarkin jama'arsa, wato Isra'ila.

7. Za ka hallaka gidan Ahab, maigidanka, domin in ɗau fansar jinin annabawa bayinsa, da fansar jinin sauran bayin Ubangiji a kan Yezebel.

8. Gama dukan gidan Ahab zai hallaka. Zan datse wa Ahab kowane ɗa namiji, bawa ko 'yantacce, cikin Isra'ila.

9. Zan mai da gidan Ahab kamar gidan Yeroboam ɗan Nebat, da kuma kamar gidan Ba'asha ɗan Ahija.

Karanta cikakken babi 2 Sar 9