Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

2 Sar 7:17-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

17. Sarki kuwa ya sa dogari wanda ya raka shi wajen Elisha ya tsare ƙofar birnin. Sai mutane suka tattake shi a ƙofar har ya mutu, kamar yadda annabi Elisha ya faɗa sa'ad da sarki ya tafi wurinsa.

18. Ya faru daidai yadda annabi Elisha ya ce wa sarki, “Za a sayar da mudu biyu na sha'ir, da mudu na lallausan gari a bakin shekel ɗaya ɗaya gobe war haka a ƙofar birnin Samariya.”

19. Dogarin ya ce wa Elisha, “Ko da Ubangiji da kansa zai buɗe tagogin sama, wannan abu zai yiwu ke nan?”Elisha kuwa ya ce, “Za ka gani da idanunka amma ba za ka ci ba.”

20. Haka kuwa ya zama gama mutane suka tattake shi a ƙofar har ya mutu.

Karanta cikakken babi 2 Sar 7