Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

2 Sar 4:1-5 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Matar wani daga cikin ƙungiyar annabawa da ya rasu, ta kai kuka wurin Elisha, ta ce, “Maigidana, baranka, wato mijina, ya rasu, ka kuwa sani shi mai tsoron Ubangiji ne, amma wanda yake binsa bashi ya zo zai kwashe 'ya'yana biyu su zama bayinsa.”

2. Sai Elisha ya ce mata, “Me zan yi miki? Ki faɗa mini abin da kike da shi a gida.”Ta ce, “Ni dai ba ni da kome a cikin gidan, sai dai kurtun mai.”

3. Sa'an nan ya ce mata, “Ki tafi ki yi aron tandaye da yawa daga maƙwabtanki waɗanda ba kome a ciki.

4. Sa'an nan ki shiga ɗaki, ke da 'ya'yanki, ku rufe ƙofa. Ki ɗura mai cikin tandayen nan duka, bi da bi.”

5. Sai ta tashi daga wurinsa, ta tafi ta shiga ɗaki tare da 'ya'yanta, ta rufe ƙofar. 'Ya'yan suna kawo tandaye tana ɗurawa.

Karanta cikakken babi 2 Sar 4