Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

2 Sam 23:6-15 Littafi Mai Tsarki (HAU)

6. Amma marasa Allah suna kama da ƙayayuwan da aka zubar,

7. Amma wanda zai taɓa su, sai da wani ƙarfe ko da māshi,Za a ƙone su ƙurmus.”

8. Ga sunayen jarumawan Dawuda, Yosheb-basshebet, daga Takemon, shi ne ɗaya daga cikin shugabanni uku. Ya girgiza māshinsa, ya kashe mutum ɗari takwas baki ɗaya.

9. Wanda yake biye da shi a cikin su uku ɗin shi ne Ele'azara, ɗan Dodo, ɗan Ahowa. Yana tare da Dawuda sa'ad da suka raina Filistiyawan da suka taru don yaƙi. Mutanen Isra'ila kuwa suka jā baya,

10. shi kuwa ya tsaya, ya yi ta yaƙi da Filistiyawa, har hannunsa ya ƙage, har bai iya ɓanɓaruwa daga takobinsa ba. Ubangiji ya ba da babbar nasara a wannan rana. Bayan an gama sai Isra'ilawa suka koma wurin Ele'azara don su kwashi ganima kawai.

11. Biye da Ele'azara kuma, sai Shamma, ɗan Agi, daga Harod. Filistiyawa suka taru a Lihai, inda akwai wata gonar wake. Isra'ilawa kuwa suka guji wa Filistiyawa.

12. Amma Shamma ya tsaya a tsakiyar gonar, ya kāre ta. Ya kuma kashe Filistiyawa. Ubangiji ya ba da babbar nasara.

13. Sai jarumawa uku daga cikin jarumawa talatin, suka tafi wurin Dawuda a kogon Adullam, gab da lokacin girbi. A lokacin kuwa Filistiyawa sun kafa sansani a kwarin Refayawa.

14. Dawuda yana cikin kagara, ƙungiyar sojojin Filistiyawa kuwa tana a Baitalami.

15. Dawuda ya ji marmari, ya ce, “Kai, da ma wani zai ba ni ruwan rijiyar ƙofar garin Baitalami in sha!”

Karanta cikakken babi 2 Sam 23