Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

2 Sam 23:1-6 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Wannan ita ce maganar Dawuda ta ƙarshe. Dawuda ɗan Yesse, shi ne mutumin da Allah ya ɗaukaka, wanda Allah na Yakubu ya zaɓa ya zama sarki, wanda kuma ya shirya waƙoƙin Isra'ila. Dawuda ya ce,

2. “Ruhun Ubangiji ya yi magana ta wurina,Saƙonsa yana kan leɓunana.

3. Allah na Isra'ila ya yi magana,Matsaron Isra'ila ya ce mini,‘Sarkin da yake mulkin mutane da adalci,Wanda yake mulki da tsoron Allah,

4. Yana kama da hasken rana a kan girgijen alfijir,Rana da take sa ciyawa ta yi ƙyalƙyali bayan an gama ruwan sama.’

5. “Haka Allah zai sa wa zuriyata albarka,Gama ya yi mini madawwamin alkawari,Duka kuwa a shirye yake, zai kuwa kiyaye.Abin da nake bukata ke nan,Wannan ne nasarata,Na tabbata kuwa Allah zai kammala shi.

6. Amma marasa Allah suna kama da ƙayayuwan da aka zubar,

Karanta cikakken babi 2 Sam 23