Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

2 Sam 21:6-14 Littafi Mai Tsarki (HAU)

6. Sai ka ba mu 'ya'yansa maza bakwai domin mu rataye su a gaban Ubangiji a Gibeya a kan dutsen Ubangiji.”Sarki kuwa ya ce, “To, zan bayar.”

7. Amma sarki ya ware Mefiboshet, ɗan Jonatan, wato jikan Saul, saboda rantsuwar da yake tsakaninsa da Jonatan, ɗan Saul.

8. Sai sarki ya sa aka kamo masa Armoni da Mefiboshet, 'ya'yan Saul waɗanda Rizfa, 'yar Aiya, ta haifa masa, da 'ya'ya maza biyar na Adriyel, ɗan Barzillai, mutumin Abelmehola, waɗanda matarsa Merab 'yar Saul ta haifa masa.

9. Sarki kuwa ya bai wa Gibeyonawa su. Sai suka rataye su a kan dutse a gaban Ubangiji. Su bakwai ɗin nan suka hallaka gaba ɗaya. An kashe su a farkon kakar sha'ir.

10. Rizfa kuwa, 'yar Aiya, ta ɗauki algarara ta yi wa kanta shimfiɗa a kan dutsen. Ta zauna a wurin tun daga farkon kaka har zubar ruwan damuna da ya bugi gawawwakin. Ba ta bar tsuntsaye su sauka a kansu da rana ba, ko namomin jeji da dare.

11. Sa'ad da aka sanar wa Dawuda abin da Rizfa, 'yar Aiya, ƙwarƙwarar Saul ta yi,

12. Dawuda ya tafi ya kwaso ƙasusuwan Saul da na ɗansa Jonatan daga wurin mutanen Yabesh a Gileyad. (Gama suka sace su daga dandalin Bet-sheyan, a inda Filistiyawa suka rataye su, a ranar da suka kashe Saul a Gilbowa.)

13. Daga can ne ya kwaso ƙasusuwan Saul da na Jonatan, suka kuma tattara ƙasusuwan waɗanda aka rataye.

14. Aka binne ƙasusuwan Saul da na ɗansa Jonatan a kabarin Kish, tsohon Saul, a Zela a ƙasar Biliyaminu. Aka aikata dukan abin da sarki ya umarta. Bayan haka Allah ya ji addu'arsu a kan ƙasar.

Karanta cikakken babi 2 Sam 21