Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

2 Sam 16:19-23 Littafi Mai Tsarki (HAU)

19. Banda haka ma, wane ne ya kamata in bauta wa, in ba ɗan ubangidana ba? Kamar yadda na bauta wa tsohonka, haka kuma zan bauta maka.”

20. Sa'an nan Absalom ya juya wajen Ahitofel, ya ce, “To, ka kawo shawararka a kan abin da ya kamata mu yi?”

21. Ahitofel kuwa ya ce wa Absalom, “Ka shiga ka kwana, da ƙwarakwaran tsohonka waɗanda ya bar su su lura da gidan. Dukan Isra'ilawa za su sani ba shiri kuma tsakaninka da tsohonka. Dukan masu goyon bayanka kuma za su ƙara ƙarfafa.”

22. Sai suka kafa wa Absalom alfarwa a bisa kan soro, ya shiga ya kwana da ƙwaraƙwaran tsohonsa, a idon mutanen Isra'ila duka.

23. Shawarar da Ahitofel yake bayarwa a lokacin nan ta zama kamar faɗar Allah ce. Absalom duk da Dawuda, shawarar Ahitofel suke bi.

Karanta cikakken babi 2 Sam 16