Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Tar 29:8-13 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. Dukan waɗanda suke da duwatsu masu daraja suka bayar da su cikin taskar Haikalin Ubangiji, ta hannun Yehiyel Bagershone.

9. Sai jama'a suka yi murna da ganin yadda suka bayar hannu sake, gama sun kawo sadakokinsu a gaban Ubangiji da zuciya ɗaya, shi sarki Dawuda kuma ya yi murna ƙwarai.

10. Dawuda ya yabi Ubangiji a gaban dukan taron, ya ce, “Ya Ubangiji Allah na kakanmu Yakubu, yabo ya tabbata gare ka har abada abadin!

11. Girma, da iko, da daraja, da nasara, da ɗaukaka duk naka ne, ya Ubangiji, gama dukan abin da yake cikin sammai da duniya naka ne. Mulki kuma naka ne, ya Ubangiji. Kai ne Maɗaukaki duka.

12. Dukan wadata da girma daga gare ka suke, kai kake mulki da dukan iko da ƙarfi. Kai ne kake da iko ka ba mutum iko da ƙarfi.

13. Yanzu ya Allahnmu, muna gode maka muna kuma yabon sunanka mai daraja.

Karanta cikakken babi 1 Tar 29