Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Tar 21:26-28 Littafi Mai Tsarki (HAU)

26. Dawuda ya gina wa Ubangiji bagade a wurin, ya miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama. Sai ya yi roƙo ga Ubangiji, Ubangiji kuwa ya amsa masa ta wurin wutar da ta sauko daga sama a bisa bagaden hadayar ta ƙonawa.

27. Sa'an nan Ubangiji ya umarci mala'ikan, shi kuwa ya mai da takobinsa a kube.

28. Da Dawuda ya ga Ubangiji ya amsa masa a masussukar Arauna Bayebuse, sai ya miƙa hadaya a wurin.

Karanta cikakken babi 1 Tar 21