Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Tar 16:9-26 Littafi Mai Tsarki (HAU)

9. Ku raira masa waƙa, ku raira yabo gare shi,Ku faɗi dukan abubuwa masu banmamaki da ya yi!

10. Ku yi murna saboda mu nasa ne,Ku yi murna dukanku da kuke bauta wa Ubangiji!

11. Ku je wurin Ubangiji neman taimako,Ku tsaya a gabansa koyaushe.

12. Ku tuna da mu'ujizansa masu girma, masu banmamaki,Ku tuna kuma da hukuntai waɗanda ya yanke.

13. Ya ku zuriyar bawansa Ibrahim,Ya ku zuriyar zaɓaɓɓensa Yakubu.

14. Shi Ubangiji, shi ne Allahnmu,Umarnansa domin dukan duniya ne.

15. Zai cika alkawarinsa har abada,Alkawaransa kuma don dubban zamanai,

16. Yarjejeniyar da ya yi da Ibrahim,Da alkawarin da ya yi wa Ishaku.

17. Ubangiji ya yi madawwamin alkawari da Isra'ila,Ya yi madawwamiyar yarjejeniya da Yakubu sa'ad da ya ce,

18. “Zan ba ka ƙasar Kan'ana,Za ta zama mallakarka.”

19. Jama'ar Ubangiji kima ne,Baƙi ne kuwa a ƙasar.

20. Suka yi ta yawo daga ƙasa zuwa ƙasa,Daga wannan mulki zuwa wancan.

21. Amma bai yarda kowa ya zalunce su ba,Ya tsauta wa sarakuna da yawa saboda su.

22. Ya ce, “Kada ku taɓa bayina, zaɓaɓɓu,Kada ku cuci annabawana!”

23. Ku raira waƙa ga Ubangiji, ku dukan duniya,Ku yi shelar albishir na ceton da ya yi mana kowace rana.

24. Ku yi shelar ɗaukakarsa ga al'ummai,Da ayyukansa masu girma ga dukan mutane,

25. Ubangiji da girma yake, wajibi ne mu yabe shi,Dole mu yi tsoronsa fiye da dukan alloli.

26. Gama allolin dukan sauran al'umma gumaka ne,Amma Ubangiji shi ne ya halitta sammai.

Karanta cikakken babi 1 Tar 16