Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Tar 16 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Suka fa shigo da akwatin alkawarin Allah, suka ajiye shi a cikin alfarwar da Dawuda ya kafa masa, suka miƙa hadayu na ƙonawa da na salama a gaban Allah.

2. Da Dawuda ya gama miƙa hadayar ƙonawa da ta salama, sai ya sa wa jama'a albarka da sunan Ubangiji.

3. Ya kuma rarraba wa Isra'ilawa mata da maza, gurasa, da gunduwar nama, da kauɗar zabibi.

4. Ya kuma sa waɗansu Lawiyawa su yi hidima a gaban akwatin alkawarin Ubangiji, su ɗaukaka Ubangiji Allah na Isra'ila, su gode masa, su kuma yabe shi.

5. Asaf shi ne shugaba, na biye da shi su ne Zakariya da Aziyel, da Shemiramot, da Yehiyel, da Mattitiya, da Eliyab, da Benaiya, da Obed-edom, da Yehiyel, waɗanda za su kaɗa molaye da garayu. Asaf kuwa shi ne mai kaɗa kuge.

6. Benaiya da Yahaziyel firistoci, su ne za su riƙa busa ƙaho a gaban akwatin alkawarin Allah.

Waƙar Yabo ta Dawuda

7. A wannan lokaci ne Dawuda ya fara sa Asaf da 'yan'uwansa su riƙa raira waƙoƙin yabo ga Ubangiji.

8. Ku yi godiya ga Ubangiji, ku yi shelar girmansa,Ku sanar wa sauran al'umma abubuwan da ya yi!

9. Ku raira masa waƙa, ku raira yabo gare shi,Ku faɗi dukan abubuwa masu banmamaki da ya yi!

10. Ku yi murna saboda mu nasa ne,Ku yi murna dukanku da kuke bauta wa Ubangiji!

11. Ku je wurin Ubangiji neman taimako,Ku tsaya a gabansa koyaushe.

12. Ku tuna da mu'ujizansa masu girma, masu banmamaki,Ku tuna kuma da hukuntai waɗanda ya yanke.

13. Ya ku zuriyar bawansa Ibrahim,Ya ku zuriyar zaɓaɓɓensa Yakubu.

14. Shi Ubangiji, shi ne Allahnmu,Umarnansa domin dukan duniya ne.

15. Zai cika alkawarinsa har abada,Alkawaransa kuma don dubban zamanai,

16. Yarjejeniyar da ya yi da Ibrahim,Da alkawarin da ya yi wa Ishaku.

17. Ubangiji ya yi madawwamin alkawari da Isra'ila,Ya yi madawwamiyar yarjejeniya da Yakubu sa'ad da ya ce,

18. “Zan ba ka ƙasar Kan'ana,Za ta zama mallakarka.”

19. Jama'ar Ubangiji kima ne,Baƙi ne kuwa a ƙasar.

20. Suka yi ta yawo daga ƙasa zuwa ƙasa,Daga wannan mulki zuwa wancan.

21. Amma bai yarda kowa ya zalunce su ba,Ya tsauta wa sarakuna da yawa saboda su.

22. Ya ce, “Kada ku taɓa bayina, zaɓaɓɓu,Kada ku cuci annabawana!”

23. Ku raira waƙa ga Ubangiji, ku dukan duniya,Ku yi shelar albishir na ceton da ya yi mana kowace rana.

24. Ku yi shelar ɗaukakarsa ga al'ummai,Da ayyukansa masu girma ga dukan mutane,

25. Ubangiji da girma yake, wajibi ne mu yabe shi,Dole mu yi tsoronsa fiye da dukan alloli.

26. Gama allolin dukan sauran al'umma gumaka ne,Amma Ubangiji shi ne ya halitta sammai.

27. Daraja da ɗaukaka suna kewaye da shi,Iko da farin ciki sun cika haikalinsa.

28. Ku yi yabon Ubangiji, ku dukan mutanen duniya,Ku yabi ɗaukakarsa da ikonsa!

29. Ku yabi sunan Ubangiji mai daraja,Kuna kawo sadaka, kuna zuwa Haikalinsa.Ku rusuna a gaban Mai Tsarki da sahihiyar zuciya,

30. Ku yi rawar jiki a gabansa, ku dukan duniya!Hakika duniya ta kahu sosai, ba za ta jijjigu ba.

31. Duniya da sararin sama, ku yi farin ciki!Ku faɗa wa al'ummai, Ubangiji shi ne sarki.

32. Ki yi ruri, ke teku, da dukan abin da yake cikinki,Ka yi farin ciki, kai saura da dukan abin da yake cikinka.

33. Itatuwa a jeji za su yi sowa domin murnaSa'ad da Ubangiji zai zo ya yi mulki a duniya.

34. Ku yi godiya ga Ubangiji, gama shi nagari ne,Ƙaunarsa madawwamiya ce!

35. Ku ce masa, “Ka cece mu, ya Allah Mai Cetonmu,Ka tattara mu, ka kuɓutar da mu daga al'ummai,Domin mu gode maka,Mu kuma yabi sunanka mai tsarki.”

36. Ku yabi Ubangiji Allah na Isra'ila!Ku yi ta yabonsa har abada abadin!Sa'an nan dukan jama'a suka ce, “Amin, Amin,” suka yabi Ubangiji.

An Zaɓi Lawiyawa domin Akwatin Alkawari

37. Dawuda ya sa Asaf tare da 'yan'uwansa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji domin a yi hidima kullayaumin a gaban akwatin alkawarin kamar yadda aka bukaci a yi kowace rana.

38. Akwai kuma masu tsaron ƙofofi, wato Obed-edom ɗan Yedutun tare da 'yan'uwansa, su sittin da takwas, da Hosa.

39. Sai ya bar Zadok firist da 'yan'uwansa firistoci a wurin zama na Ubangiji a tudun da yake a Gibeyon.

40. Kowace safiya da maraice suna miƙa hadayu na ƙonawa ga Ubangiji a bisa bagaden ƙona hadaya, kamar yadda aka rubuta a dokokin Ubangiji, waɗanda ya ba Isra'ilawa.

41. Tare da su kuma akwai Heman, da Yedutun, da sauran waɗanda aka zaɓa musamman domin su yi godiya ga Ubangiji saboda madawwamiyar ƙaunarsa.

42. Heman da Yedutun suna lura da ƙaho, da kuge, da sauran kayan bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe, waɗanda ake amfani da su lokacin raira waƙoƙin yabo ga Allah. 'Ya'yan Yedutun, maza, su aka ba aikin tsaron ƙofa.

43. Sa'an nan dukan jama'a suka watse, kowa ya koma gidansa, Dawuda kuma ya koma gidansa, ya sa wa iyalinsa albarka.