Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Tar 16:21-30 Littafi Mai Tsarki (HAU)

21. Amma bai yarda kowa ya zalunce su ba,Ya tsauta wa sarakuna da yawa saboda su.

22. Ya ce, “Kada ku taɓa bayina, zaɓaɓɓu,Kada ku cuci annabawana!”

23. Ku raira waƙa ga Ubangiji, ku dukan duniya,Ku yi shelar albishir na ceton da ya yi mana kowace rana.

24. Ku yi shelar ɗaukakarsa ga al'ummai,Da ayyukansa masu girma ga dukan mutane,

25. Ubangiji da girma yake, wajibi ne mu yabe shi,Dole mu yi tsoronsa fiye da dukan alloli.

26. Gama allolin dukan sauran al'umma gumaka ne,Amma Ubangiji shi ne ya halitta sammai.

27. Daraja da ɗaukaka suna kewaye da shi,Iko da farin ciki sun cika haikalinsa.

28. Ku yi yabon Ubangiji, ku dukan mutanen duniya,Ku yabi ɗaukakarsa da ikonsa!

29. Ku yabi sunan Ubangiji mai daraja,Kuna kawo sadaka, kuna zuwa Haikalinsa.Ku rusuna a gaban Mai Tsarki da sahihiyar zuciya,

30. Ku yi rawar jiki a gabansa, ku dukan duniya!Hakika duniya ta kahu sosai, ba za ta jijjigu ba.

Karanta cikakken babi 1 Tar 16