Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Tar 16:1-8 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Suka fa shigo da akwatin alkawarin Allah, suka ajiye shi a cikin alfarwar da Dawuda ya kafa masa, suka miƙa hadayu na ƙonawa da na salama a gaban Allah.

2. Da Dawuda ya gama miƙa hadayar ƙonawa da ta salama, sai ya sa wa jama'a albarka da sunan Ubangiji.

3. Ya kuma rarraba wa Isra'ilawa mata da maza, gurasa, da gunduwar nama, da kauɗar zabibi.

4. Ya kuma sa waɗansu Lawiyawa su yi hidima a gaban akwatin alkawarin Ubangiji, su ɗaukaka Ubangiji Allah na Isra'ila, su gode masa, su kuma yabe shi.

5. Asaf shi ne shugaba, na biye da shi su ne Zakariya da Aziyel, da Shemiramot, da Yehiyel, da Mattitiya, da Eliyab, da Benaiya, da Obed-edom, da Yehiyel, waɗanda za su kaɗa molaye da garayu. Asaf kuwa shi ne mai kaɗa kuge.

6. Benaiya da Yahaziyel firistoci, su ne za su riƙa busa ƙaho a gaban akwatin alkawarin Allah.

7. A wannan lokaci ne Dawuda ya fara sa Asaf da 'yan'uwansa su riƙa raira waƙoƙin yabo ga Ubangiji.

8. Ku yi godiya ga Ubangiji, ku yi shelar girmansa,Ku sanar wa sauran al'umma abubuwan da ya yi!

Karanta cikakken babi 1 Tar 16