Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Tar 15:2-12 Littafi Mai Tsarki (HAU)

2. Sai Dawuda ya ce, “Kada wani ya ɗauki akwatin alkawari na Allah sai Lawiyawa kaɗai, gama su ne Ubangiji ya zaɓa domin su riƙa ɗaukar akwatin alkawarin Ubangiji, su kuma yi masa hidima har abada.”

3. Saboda haka Dawuda ya tattara Isra'ilawa duka a Urushalima don a kawo akwatin alkawarin Ubangiji a wurinsa, inda aka riga aka shirya masa.

4. Dawuda kuma ya tattara zuriyar Haruna a wuri ɗaya, tare kuma da Lawiyawa.

5. Waɗanda aka tattaro ke nan, daga iyalin Kohat su ɗari da shirin ne. Uriyel shi ne shugabansu.

6. Daga iyalin Merari su ɗari biyu da ashirin, Asaya ne shugabansu.

7. Daga iyalin Gershon ɗari da talatin, Yowel ne shugabansu.

8. Daga iyalin Elizafan ɗari biyu, Shemaiya ne shugabansu.

9. Daga iyalin Hebron su tamanin, Eliyel ne shugabansu.

10. Daga iyalin Uzziyel ɗari da goma sha biyu, Amminadab ne shugabansu.

11. Sa'an nan Dawuda ya kira Zadok da Abiyata firistoci, da Lawiyawa, wato Uriyel, da Asaya, da Yowel, da Shemaiya, da Eliyel, da Amminadab,

12. ya ce musu, “Ku ne shugabanni na gidajen kakanninku, Lawiyawa. Sai ku tsarkake kanku da 'yan'uwanku domin ku iya kawo akwatin alkawarin Allah na Isra'ila a inda na shirya masa.

Karanta cikakken babi 1 Tar 15