Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Sar 21:1-9 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Nabot Bayezreyele yana da gonar inabi a Yezreyel kusa da fādar Ahab, Sarkin Samariya.

2. Sai Ahab ya yi magana da Nabot ya ce, “Ka ba ni gonar inabinka don in mai da ita lambu, gama gonar tana kusa da gidana, ni kuwa zan ba ka wata gonar inabi a maimakonta, idan kuma kana so, sai in ba ka tamanin kuɗinta.”

3. Amma Nabot ya ce wa Ahab, “Ubangiji ya sawwaƙa in ba ka gādon kakannina.”

4. Ahab ya koma gida da baƙin ciki da rai a ɓace saboda abin da Nabot Bayezreyele ya faɗa masa. Ahab ya kwanta a gadonsa, ya mai da fuskarsa bango ya ƙi cin abinci.

5. Yezebel, matarsa kuwa ta zo wurinsa, ta ce masa, “Me ya sa ka damu, ka ruɗe haka, har ka ƙi cin abinci?”

6. Ya ce mata, “Domin na yi magana da Nabot Bayezreyele, na ce ya sayar mini da gonar inabinsa, idan kuma yana so, sai in ba shi wata gonar inabi a maimakon tasa, amma ya ce ba zai ba ni gonar inabin ba.”

7. Yezebel, matarsa, ta ce masa, “Ba kai ne kake mulkin Isra'ila ba? Tashi, ka ci abinci, ka yi farin ciki, zan ba ka gonar inabin Nabot Bayezreyele.”

8. Sa'an nan ta rubuta wasiƙu da sunan Ahab, ta hatimce su da hatiminsa, sa'an nan ta aika da wasiƙun zuwa ga dattawa da fādawan da suke zaune a birnin tare da Nabot.

9. Ta rubuta a wasiƙun, “A yi shelar azumi, a sa Nabot a gaban jama'a.

Karanta cikakken babi 1 Sar 21