Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Sar 2:6-13 Littafi Mai Tsarki (HAU)

6. Ka san abin da za ka yi, kada ka bar shi ya mutu ta hanyar lafiya.

7. “Amma ka nuna alheri ga 'ya'yan Barzillai daga Gileyad, ka lura da su da kyau, gama sun nuna mini alheri sa'ad da nake gudu daga ɗan'uwanka, Absalom.

8. “Ga kuma Shimai ɗan Gera, daga garin Bahurim ta Biliyaminu. Shi ne ya yi mini mugun zagi sa'ad da na tafi Mahanayim, amma sa'ad da ya zo taryata a Urdun, sai na rantse masa da Ubangiji, na ce ba zan kashe shi ba.

9. Don haka dole ka hukunta shim, ka dai san abin da za ka yi da shi, lalle ne kuma za ka ga an kashe shi.”

10. Sa'an nan Dawuda ya rasu, aka binne shi a birnin Urushalima.

11. Ya yi shekara arba'in yana sarautar Isra'ila. Ya yi mulki shekara bakwai a Hebron, sa'an nan ya yi shekara talatin da uku yana mulki a Urushalima.

12. Sulemanu kuwa ya hau gadon sarautar ubansa, Dawuda. Mulkinsa kuma ya kahu sosai.

13. Sa'an nan Adonija ɗan Haggit ya tafi wurin Bat-sheba, tsohuwar Sulemanu. Ta ce masa, “Ka zo lafiya?”Ya ce, “Lafiya lau.”

Karanta cikakken babi 1 Sar 2