Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Sar 16:1-6 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Ubangiji ya yi magana da Yehu, ɗan Hanani a kan Ba'asha, ya ce,

2. “Tun da yake na ɗauke ka daga cikin ƙura, na maishe ka shugaban jama'ata Isra'ila, kai kuwa ka bi hanyar Yerobowam, ka sa jama'ata, wato Isra'ila, su yi zunubi, suka sa na yi fushi saboda zunubansu,

3. to, zan shafe ka da gidansa, in mai da gidanka kamar gidan Yerobowam ɗan Nebat.

4. Duk mutumin da yake naka da zai mutu a cikin birni, karnuka ne za su cinye shi. Wanda kuma ya mutu a saura, tsuntsaye ne za su cinye shi.”

5. Sauran ayyukan Ba'asha, da dukan abin da ya yi, da irin ƙarfinsa, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Isra'ila.

6. Ba'asha kuwa ya rasu, aka binne shi a Tirza. Sai Ila, ɗansa ya gāji sarautarsa.

Karanta cikakken babi 1 Sar 16