Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Sam 25:38-44 Littafi Mai Tsarki (HAU)

38. Bayan kwana goma sai Ubangiji ya bugi Nabal, ya mutu.

39. Sa'ad da Dawuda ya ji Nabal ya mutu, sai ya ce, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji wanda ya sāka mini a kan irin rainin da Nabal ya yi mini. Ya kuma hana ni aikata mugunta. Ya ɗora wa Nabal muguntarsa a kansa.”Sa'an nan Dawuda ya aika, ya nemi Abigail ta zama matarsa.

40. Da barorin Dawuda suka zo wurin Abigail a Karmel, suka ce mata, “Dawuda ne ya aiko mu wurinki domin mu kai ki wurinsa, ki zama matarsa.”

41. Sai ta rusuna har ƙasa, ta ce, “Ni baranyarsa ce, ina a shirye in wanke ƙafafun barorinsa.”

42. Sai ta yi hanzari ta hau jaki, ta ɗauki kuyanginta, su biyar, ta tafi tare da manzannin Dawuda, ta zama matarsa.

43. Dawuda kuma ya auro Ahinowam Bayezreyeliya, dukansu biyu kuwa suka zama matansa.

44. Amma Saul ya aurar da Mikal, 'yarsa, matar Dawuda, ga Falti ɗan Layish wanda yake a Gallim.

Karanta cikakken babi 1 Sam 25