Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Sam 25:1-5 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Sama'ila kuwa ya rasu. Dukan Isra'ilawa suka taru suka yi makoki dominsa. Suka binne shi a gidansa a Rama.Sai Dawuda ya tashi ya tafi jejin Faran.

2. Akwai wani mutumin Mawon wanda yake da harka a Karmel. Mutumin mai dukiya ne ƙwarai, yana da tumaki dubu uku (3,000) da awaki dubu (1,000). Yana yi wa tumakinsa sausaya a Karmel.

3. Sunan mutumin kuwa Nabal, sunan matarsa kuma Abigail, ita haziƙa ce, kyakkyawa, amma mijinta miskili ne, marar mutunci. Shi daga zuriyar Kalibu ne.

4. Daga cikin jeji, Dawuda ya ji, wai Nabal yana yi wa tumakinsa sausaya,

5. sai ya aiki samari goma, ya ce musu, “Ku tafi Karmel wurin Nabal, ku ce ina gaishe shi.

Karanta cikakken babi 1 Sam 25