Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Sam 1:24-28 Littafi Mai Tsarki (HAU)

24. Sa'ad da ta yaye yaron, sai ta ɗauke shi, ta kuma ɗauki bijimi bana uku, da mudun gari, da salkar ruwan inabi, ta kai shi ɗakin Ubangiji a Shilo, yaron kuwa yana ɗan ƙarami.

25. Sai suka yanka bijimin, suka kuma kai yaron wurin Eli.

26. Sa'an nan Hannatu ta ce, “Gafara dai, ba ka tuna da ni ba? Ai, ni ce matar da ta taɓa tsayawa a gabanka, tana roƙon Ubangiji.

27. Na roƙi Ubangiji wannan yaro, Ubangiji kuwa ya biya mini bukatata da na roƙa a gare shi.

28. Saboda haka nake miƙa shi ga Ubangiji muddin ransa. Ya zama na Ubangiji.”A can ya yi wa Ubangiji sujada.

Karanta cikakken babi 1 Sam 1