Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Yah 7:36-47 Littafi Mai Tsarki (HAU)

36. Me kuma yake nufi da cewa, ‘Za ku neme ni amma ba za ku same ni ba’? da kuma cewa, ‘Inda nake ba za ku iya zuwa ba’?”

37. A ranar ƙarshe ta idin, wato babbar ranar, sai Yesu ya tsaya, ya ɗaga murya ya ce, “Duk mai jin ƙishirwa yă zo gare ni yă sha.

38. Duk mai gaskatawa da ni, kamar yadda Nassi ya ce, ‘Daga zuciyarsa ne kogunan ruwan rai za su gudana.’ ”

39. To, wannan shi ne ya faɗa game da Ruhu, wanda masu gaskatawa da shi za su karɓa, domin har yanzu ba a ba da Ruhu ba, saboda ba a ɗaukaka Yesu ba tukuna.

40. Da jin maganan nan waɗansu daga cikin taron suka ce, “Hakika wannan annabin nan ne.”

41. Waɗansu kuwa suka ce, “Wannan Almasihu ne.” Amma waɗansu suka ce, “Me? Ashe, Almasihu daga ƙasar Galili zai fito?

42. Nassi ba cewa ya yi Almasihu zuriyar Dawuda ne ba, daga kuma Baitalami yake, ƙauyen da Dawuda ya zauna?”

43. Sai kuma rabuwa ta shiga tsakaninsu a kansa.

44. Waɗansunsu suka so su kama shi, amma ba wanda ya taɓa shi.

45. Daga nan dogaran Haikali suka koma wurin manyan firistoci da Farisiyawa, su kuwa suka ce musu, “Don me ba ku kawo shi ba?”

46. Sai dogaran suka amsa suka ce, “A'a, ba mutumin da ya taɓa magana kamar wannan!”

47. Sai Farisiyawa suka amsa musu suka ce, “Af! Har ku ma an ɓad da ku ne?

Karanta cikakken babi Yah 7