Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Yah 5:25-43 Littafi Mai Tsarki (HAU)

25. “Lalle hakika, ina gaya muku, lokaci na zuwa, har ma ya yi, da matattu za su ji muryar Ɗan Allah, masu ji kuwa su rayu.

26. Yadda Uba kansa yake tushen rai, haka ya sa Ɗan ya zama tushen rai.

27. Ya kuma ba shi ikon zartar da hukunci, saboda shi Ɗan Mutum ne.

28. Kada ku yi mamakin wannan, domin lokaci na zuwa da duk waɗanda suke kaburbura za su ji murya tasa,

29. su kuma fito, waɗanda suka aikata nagarta su tashi, tashin rai, waɗanda suka yi rashin gaskiya kuwa su tashi, tashin hukunci.

30. “Ba na iya yin kome ni kaɗai. Yadda nake ji, haka nake yin hukunci. Hukuncina kuwa na adalci ne, domin ba nufin kaina nake bi ba, sai dai nufin wanda ya aiko ni.

31. In na shaida kaina, shaidata ba tabbatacciya ba ce.

32. Akwai wani mashaidina dabam, na kuwa san shaidar da yake yi mini tabbatacciya ce.

33. Kun aika wajen Yahaya, shi kuma ya shaidi gaskiya.

34. Duk da haka shaidar da na dogara da ita ba ta mutum ba ce. Na dai faɗi haka ne domin ku sami ceto.

35. Yahaya fitila ne mai ci, mai haske kuma, kun kuwa yarda ku yi farin ciki matuƙa da haskensa ɗan lokaci kaɗan.

36. Amma shaidar da ni nake da ita ta fi ta Yahaya ƙarfi. Domin ayyukan da Uba ya ba ni in gama, su ainihin ayyukan nan da nake yi, ai, su ne shaidata a kan cewa, Uba ne ya aiko ni.

37. Uban kuma da ya aiko ni, shi kansa ya shaide ni. Ba ku taɓa jin muryarsa ba, ko ganin kama tasa.

38. Maganarsa kuwa ba ta zauna a zuciyarku ba, domin ba ku gaskata wanda ya aiko ni ba.

39. Kuna ta nazarin Littattafai, don a tsammaninku a cikinsu za ku sami rai madawwami, alhali kuwa su ne suke shaidata.

40. Duk da haka, kun ƙi zuwa wurina ku sami rai.

41. Ba na karɓar girma wurin mutane.

42. Amma fa na san ku, ba ku da ƙaunar Allah a zuci.

43. Ni na zo ne da sunan Ubana, ga shi, ba ku karɓe ni ba. In da wani zai zo da sunan kansa, shi za ku karɓa.

Karanta cikakken babi Yah 5