Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Yah 4:24-42 Littafi Mai Tsarki (HAU)

24. Allah Ruhu ne, masu yi masa sujada kuwa lalle su yi masa sujada a ruhu, da gaskiya kuma.”

25. Sai matar ta ce masa, “Na san Masihi yana zuwa, wanda ake kira Almasihu. Sa'ad da ya zo kuwa, zai sanar da mu kome.”

26. Yesu ya ce mata, “Ni ne, ni mai maganan nan da yake.”

27. Nan take almajiransa suka dawo. Suka yi mamakin ganin yana magana da mace. Amma kuwa ba wanda ya ce, “Me kike bukata?” ko, “Don me kake magana da ita?”

28. Sai matar ta bar tulunta, ta koma gari, ta ce wa mutane,

29. “Ku zo, ku ga mutumin da ya gaya mini duk abin da na taɓa yi! Shin, ko wannan shi ne Almasihu?”

30. Sai suka fito daga garin suka nufo shi.

31. Ana cikin haka sai almajiran suka roƙe shi suka ce, “Ya shugaba, ci abinci.”

32. Amma ya ce musu, “Ina da abincin da ba ku sani ba.”

33. Almajiran suka ce wa juna, “Shin, wani ya kawo masa abinci ne?”

34. Sai Yesu ya ce musu, “Abincina shi ne in aikata nufin wanda ya aiko ni, in kuma cika aikinsa.

35. Ba kuna cewa, kaka saura wata huɗu ba? Ina gaya muku fa, ku duba gonaki, ku gani, sun nuna sun isa girbi.

36. Mai girbi na samun lada, yana kuma tara amfani zuwa rai madawwami, domin mai shuka da mai girbi su yi farin ciki tare.

37. A nan kam, wannan karin maganar gaskiya ne cewa, ‘Wani da shuka, wani da girbi.’

38. Na aike ku girbin abin da ba ku yi wahalarsa ba. Waɗansu sun yi wahala, ku kuwa kun mori wahalarsu.”

39. Samariyawa da yawa na wannan gari suka gaskata da shi saboda maganar matan nan da ta ce, “Ya gaya mini duk abin da na taɓa yi.”

40. Da Samariyawa suka iso wurinsa, suka roƙe shi ya sauka a wurinsu. Ya kuwa kwana biyu a nan.

41. Waɗansu kumma da yawa fiye da na dā suka ba da gaskiya saboda magana tasa.

42. Sa'an nan suka ce wa macen, “Yanzu kam, mun ba da gaskiya, ba don abin da kika faɗa kawai ba, domin mu ma mun ji da kanmu, mun kuma tabbata lalle wannan shi ne Mai Ceton duniya.”

Karanta cikakken babi Yah 4