Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Yah 3:3-10 Littafi Mai Tsarki (HAU)

3. Yesu ya amsa masa ya ce, “Lalle hakika, ina gaya maka, in ba a sāke haifar mutum ba, ba zai iya ganin Mulkin Allah ba.”

4. Nikodimu ya ce masa, “Ƙaƙa za a haifi mutum bayan ya tsufa? Wato, ya iya komawa a cikin uwa tasa ta sāke haifo shi?”

5. Yesu ya amsa masa ya ce, “Lalle hakika, ina gaya maka, in ba an haifi mutum ta ruwa da kuma Ruhu ba, ba zai iya shiga Mulkin Allah ba.

6. Abin da mutum ya haifa mutum ne, abin kuma da Ruhu ya haifa ruhu ne.

7. Kada ka yi mamaki domin na ce maka, ‘Dole a sāke haifarku.’

8. Iska tana busawa inda ta ga dama. Kakan ji motsinta, amma ba ka san inda ta fito da inda za ta. Haka fa yake ga duk wanda Ruhu ya haifa.”

9. Sai Nikodimu ya amsa masa ya ce, “Ƙaƙa wannan zai yiwu?”

10. Yesu ya amsa masa ya ce, “Ashe, kai ma da kake malamin Isra'ila, ba ka fahimci waɗannan al'amura ba?

Karanta cikakken babi Yah 3