Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Yah 3:1-4 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. To, akwai wani Bafarisiye, sunansa Nikodimu, wani shugaban Yahudawa.

2. Wannan mutum ya zo wurin Yesu da dad dare, ya ce masa, “Ya Shugaba, mun sani kai malami ne da ka zo daga wurin Allah, domin ba mai iya yin waɗannan mu'ujizan da kake yi, sai ko Allah yana tare da shi.”

3. Yesu ya amsa masa ya ce, “Lalle hakika, ina gaya maka, in ba a sāke haifar mutum ba, ba zai iya ganin Mulkin Allah ba.”

4. Nikodimu ya ce masa, “Ƙaƙa za a haifi mutum bayan ya tsufa? Wato, ya iya komawa a cikin uwa tasa ta sāke haifo shi?”

Karanta cikakken babi Yah 3