Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Yah 16:30-33 Littafi Mai Tsarki (HAU)

30. Yanzu ne muka tabbata ka san kome, ba sai wani ya tambaye ka ba. Ta haka muka gaskata daga wurin Allah ka fito.”

31. Yesu ya amsa musu ya ce, “Ashe, yanzu kun gaskata?

32. To, lokaci na zuwa, har ma ya yi, da za a warwatsa ku, kowa yă koma gidansu, ku bar ni ni kaɗai. Duk da haka kuwa ba ni kaɗai nake ba, domin Uba na tare da ni.

33. Na faɗa muku wannan ne domin a gare ni ku sami salama. A duniya kuna shan wuya, amma dai ku yi farin ciki, ai, na yi nasara da duniya.”

Karanta cikakken babi Yah 16