Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Yah 11:41-45 Littafi Mai Tsarki (HAU)

41. Sai suka kawar da dutsen. Yesu kuwa ya ɗaga kai sama ya ce, “Ya Uba, na gode maka da ka saurare ni.

42. Ko dā ma na sani koyaushe kana saurarona, amma na faɗi haka ne saboda jama'ar da suke nan tsaitsaye, domin su gaskata kai ne ka aiko ni.”

43. Da ya faɗi haka ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce, “Li'azaru fito!”

44. Sai mamacin ya fito, ƙafa da hannu a ɗaure da likkafani, fuska tasa kuma a naɗe da mayani. Yesu ya ce musu, “Ku kwance masa, ya tafi.”

45. Saboda haka Yahudawa da yawa da suka zo wurin Maryamu, suka kuma ga abin da ya yi, suka gaskata da shi.

Karanta cikakken babi Yah 11