Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Yah 10:22-32 Littafi Mai Tsarki (HAU)

22. Lokacin idin tsarkakewa ne kuwa a Urushalima,

23. damuna ce kuma, Yesu kuwa na zagawa a Shirayin Sulemanu cikin Haikali,

24. sai Yahudawa suka kewaye shi, suka ce masa, “Har yaushe za ka bar mu da shakka? In dai kai ne Almasihun, ka gaya mana a fili.”

25. Yesu ya amsa musu ya ce, “Ai, na faɗa muku, ba ku gaskata ba. Ayyukan da nake yi da sunan Ubana, suke shaidata.

26. Amma ku ba ku gaskata ba, domin ba kwa cikin tumakina.

27. Tumakin nan nawa sukan saurari muryata, na san su, suna kuma bi na.

28. Ina ba su rai madawwami, ba kuwa za su halaka ba har abada, ba kuma mai ƙwace su daga hannuna.

29. Ubana, wanda ya ba ni su, ya fi duka girma, ba kuwa mai iya ƙwace su daga ikon Uban.

30. Ni da Uba ɗaya muke.”

31. Sai Yahudawa suka sāke ɗebo duwatsu su jajjefe shi.

32. Yesu ya amsa musu ya ce, “Na nuna muku ayyuka nagari masu yawa daga wurin Uba, a kan wanne a cikinsu za ku jajjefe ni?”

Karanta cikakken babi Yah 10