Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Yah 10:20-28 Littafi Mai Tsarki (HAU)

20. Da yawa daga cikinsu suka ce, “Ai, mai iska ne, haukansa kawai yake yi. Don me za ku saurare shi?”

21. Waɗansu kuwa suka ce, “A'a, wannan magana, ai, ba ta mai iska ba ce. Ashe, iska tana iya buɗe wa makaho ido?”

22. Lokacin idin tsarkakewa ne kuwa a Urushalima,

23. damuna ce kuma, Yesu kuwa na zagawa a Shirayin Sulemanu cikin Haikali,

24. sai Yahudawa suka kewaye shi, suka ce masa, “Har yaushe za ka bar mu da shakka? In dai kai ne Almasihun, ka gaya mana a fili.”

25. Yesu ya amsa musu ya ce, “Ai, na faɗa muku, ba ku gaskata ba. Ayyukan da nake yi da sunan Ubana, suke shaidata.

26. Amma ku ba ku gaskata ba, domin ba kwa cikin tumakina.

27. Tumakin nan nawa sukan saurari muryata, na san su, suna kuma bi na.

28. Ina ba su rai madawwami, ba kuwa za su halaka ba har abada, ba kuma mai ƙwace su daga hannuna.

Karanta cikakken babi Yah 10