Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Yah 1:6-14 Littafi Mai Tsarki (HAU)

6. Akwai wani mutum da Allah ya aiko, mai suna Yahaya.

7. Shi fa ya zo shaida ne, domin ya shaidi hasken, kowa yă ba da gaskiya ta hanyarsa.

8. Ba shi ne hasken ba, ya zo ne domin ya shaidi hasken.

9. Akwai hakikanin haske mai shigowa duniya da yake haskaka kowane mutum.

10. Dā yana duniya, duniyar ta wurinsa ta kasance, duk da haka duniya ba ta san shi ba.

11. Ya zo ga abin mulkinsa ne, jama'a tasa kuwa ba ta karɓe shi ba.

12. Amma duk iyakar waɗanda suka karɓe shi, wato, masu gaskatawa da sunansa, ya ba su ikon zama 'ya'yan Allah,

13. wato, waɗanda aka haifa ba daga jini ba, ba daga nufin jiki ko nufin mutum ba, amma daga wurin Allah.

14. Kalman nan kuwa ya zama mutum, ya zauna a cikinmu, yana mai matuƙar alheri da gaskiya. Mun kuma dubi ɗaukakarsa, ɗaukaka ce ta makaɗaicin Ɗa daga wurin Ubansa.

Karanta cikakken babi Yah 1