Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Yah 1:34-41 Littafi Mai Tsarki (HAU)

34. Na kuwa gani, na kuma yi shaida, cewa wannan Ɗan Allah ne.”

35. Kashegari kuma Yahaya na tsaye da almajiransa biyu.

36. Yana duban Yesu na tafiya, sai ya ce, “Kun ga, ga Ɗan Rago na Allah!”

37. Almajiran nan biyu suka ji ya faɗi haka, sai suka bi Yesu.

38. Yesu ya waiwaya ya ga suna biye da shi, sai ya ce musu, “Me kuke nema?” Suka ce masa, “Ya Rabbi, wato Malam ke nan, ina kake da zama?”

39. Sai ya ce musu, “Ku zo ku gani.” Sai suka je suka ga inda yake da zama, suka kuwa yini tare da shi. Wajen ƙarfe huɗu na yamma ne kuwa.

40. Ɗaya daga cikin biyun nan da suka ji maganar Yahaya suka kuma bi Yesu, Andarawas ne, ɗan'uwan Bitrus.

41. Sai ya fara samo ɗan'uwansa Bitrus, ya ce masa, “Mun sami Almasihu,” wato shafaffe.

Karanta cikakken babi Yah 1