Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Yah 1:11-16 Littafi Mai Tsarki (HAU)

11. Ya zo ga abin mulkinsa ne, jama'a tasa kuwa ba ta karɓe shi ba.

12. Amma duk iyakar waɗanda suka karɓe shi, wato, masu gaskatawa da sunansa, ya ba su ikon zama 'ya'yan Allah,

13. wato, waɗanda aka haifa ba daga jini ba, ba daga nufin jiki ko nufin mutum ba, amma daga wurin Allah.

14. Kalman nan kuwa ya zama mutum, ya zauna a cikinmu, yana mai matuƙar alheri da gaskiya. Mun kuma dubi ɗaukakarsa, ɗaukaka ce ta makaɗaicin Ɗa daga wurin Ubansa.

15. Yahaya ya shaida shi, ya ɗaga murya ya ce, “Wannan shi ne wanda na ce, ‘Mai zuwa bayana ya zama shugabana, domin dā ma yana nan tun ba ni.’ ”

16. Dukanmu kuwa daga falala tasa muka samu, alheri kan alheri.

Karanta cikakken babi Yah 1