Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mat 27:1-5 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Da gari ya waye sai duk manyan firistoci da shugabannin jama'a suka yi shawara a kan Yesu su kashe shi.

2. Sai suka ɗaure shi, suka tafi da shi, suka ba da shi ga mai mulki Bilatus.

3. Sa'ad da Yahuza mai bashe shi ya ga an yanke masa hukuncin kisa, sai ya yi nadama, ya mayar wa manyan firistoci da shugabanni da kuɗi azurfa talatin ɗin nan,

4. ya ce, “Na yi zunubi da na ba da marar laifi a kashe shi.” Suka ce, “Ina ruwanmu? Kai ka jiyo!”

5. Sai ya watsar da kuɗin azurfan nan a Haikali, ya fita, ya je ya rataye kansa.

Karanta cikakken babi Mat 27