Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mat 26:70-74 Littafi Mai Tsarki (HAU)

70. Amma ya musa a gabansu duka ya ce, “Ni ban san abin da kike nufi ba.”

71. Da ya fito zaure, sai wata baranya kuma ta gan shi, ta ce wa waɗanda suke tsaitsaye a wurin, “Ai, mutumin nan tare yake da Yesu Banazare!”

72. Sai ya sāke musawa har da rantsuwa ya ce, “Ban ma san mutumin nan ba.”

73. Jim kaɗan sai na tsaitsayen suka matso, suka ce wa Bitrus, “Lalle kai ma ɗayansu ne, don irin maganarka ta tona ka.”

74. Sai ya fara la'anar kansa, yana ta rantse-rantse, yana cewa, “Ban ma san mutumin nan ba.” Nan da nan sai zakara ya yi cara.

Karanta cikakken babi Mat 26