Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mat 26:14-17 Littafi Mai Tsarki (HAU)

14. Sai ɗaya daga cikin sha biyun nan, mai suna Yahuza Iskariyoti, ya je wurin manyan firistoci,

15. ya ce, “Me za ku ba ni, in na bashe shi a gare ku?” Sai suka ƙirga kuɗi azurfa talatin, suka ba shi.

16. Tun daga lokacin nan ne ya riƙa neman hanyar da zai bashe shi.

17. To, a ranar farko ta idin abinci marar yisti sai almajiran suka zo wurin Yesu suka ce, “Ina kake so mu shirya maka cin Idin Ƙetarewa?”

Karanta cikakken babi Mat 26